Luke 6

Ubangijin Asabbaci

1A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci. 2Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?” 3Yesu ya amsa musu, ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, saʼad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba? 4Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, saʼan nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?” 5Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”

6A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majamiʼa yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye. 7Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa. 8Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.

9Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci: a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”

10Sai ya kalle su duka, saʼan nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye. 11Amma suka fusata, suka fara shawara da junansu a kan abin da za su yi da Yesu.

Manzanni Sha Biyu

12Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yǎ yi adduʼa, ya kuma kwana yana adduʼa ga Allah. 13Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni: 14Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗanʼuwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu, 15Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot, 16Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.

Albarku da Laʼanu

17Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga koʼina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku, 18waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su. 19Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.

20Da ya dubi almajiransa, sai ya ce,

“Masu albarka ne ku da kuke matalauta,
gama mulkin Allah naku ne.
21Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu,
gama za ku ƙoshi.
Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu,
gama za ku yi dariya.
22Masu albarka ne saʼad da mutane suka ƙi ku,
suka ware ku, suka zage ku,
suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
23“Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.

24“Amma kaitonku da kuke da arziki,
gama kun riga kun sami taʼaziyyarku.
25Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu,
gama za ku zauna da yunwa.
Kaitonku da kuke dariya yanzu,
gama za ku yi makoki da kuka.
26Kaitonku saʼad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku,
gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.

Ƙaunar Abokan Gāba

27“Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na: Ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri. 28Ku albarkaci waɗanda suke laʼanta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku adduʼa. 29In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa ʼyar cikin ma. 30Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yǎ mayar maka. 31Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.

32“In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko ‘masu zunubi’ ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu. 33In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko ‘masu zunubi’ ma suna yin haka. 34In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyanka ne kawai, ina ribar wannan? Ko ‘masu zunubi’ ma, suna ba da bashi ga ‘masu zunubi’, da fata za a biya su tsab. 35Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama ʼyaʼyan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye. 36Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.

Ba wa Waɗansu Laifi

37“Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku. 38Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yǎ yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”

39Ya kuma faɗa musu wannan misali, cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba? 40Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.

41“Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗanʼuwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba? 42Yaya za ka ce wa ɗanʼuwanka, ‘Ɗanʼuwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, saʼan nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗanʼuwanka.”

Itace da ʼYaʼyansa

43“Ba itace mai kyau da yake ba da munanan ʼyaʼya. Mummunan itace kuma ba ya ba da ʼyaʼya masu kyau. 44Kowane itace da irin ʼyaʼyansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke ʼyaʼyan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa ʼyaʼyan inabi daga sarƙaƙƙiya. 45Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”

Mai Gini Mai Hikima da Mai Gini Marar Hikima

46“Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa? 47Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yǎ ji kalmomina, yǎ kuma aikata. 48Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, saʼan nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi. 49Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A saʼad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yǎ rushe, mummunar rushewa kuwa.”

Copyright information for HauSRK